Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

An bukaci a biya diyan mahakan Ma’adanai a Marikana

Iyalan mahaka ma’adanan karkashin kasa da Jami’an ‘yan Sanda suka yi wa kisan kiyashi a garin Marikana na Kasar Afrika ta kudu sun bukaci gwamanati ta biya su diya bayan wani bincike da aka gudanar.

Wasu daga cikin Iyalan wadanda aka kashe a Marikana.
Wasu daga cikin Iyalan wadanda aka kashe a Marikana. AFP PHOTO / GORDON HARNOLS
Talla

Kisan kiyashin na garin marikana daya yi sanadiyar mutuwar mahaka ma’adinan karkashin kasa 34, ya faru ne a shekara ta 2012 yayin da iyalansu da wadanda aka raunata a harin suka bukaci gwamanati ta biya su diya, kamar yadda lawyan da ya tsaya musu mai suna Dali Mpofu ya bayyana.

Lauyan ya ce zai shigar da kara a kotu game da wannan batun kafin sake zagoyawar ranar tunawa da aukuwar lamarin karo na uku.

An dai danganta wannan kisan a matasyin mafi muni tun bayan kawo karshen mulkin wariyar launin fata a kasar  Afrika ta kudu shekaru 20 da suka gabata.

Lauyan da ke wakiltan mutane 300 a kan wannan batun ya bayyana cewa, ya zama dole a shigar da karar kafin ranar 16 ga watan Agustan wannan Shekarar.

Tuni dai iyalan mamatan da wadanda aka jikata suka bayyana bacin ransu, saboda wanke manyan jami’an gwamanti da ake zarginsu da hannu a aikata laifin kisan yayin da kuma bincike ya nuna cewa kananan Jami’an 'yan sanda kawai ne ke da laifi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.