Isa ga babban shafi
Najeriya-Kamaru

Boko Haram : Buhari zai kai ziyara Kamaru bayan Azumi

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da goron gayyata da Shugaban Paul Biya ya aiko ma sa zuwa Kamaru domin tattauna batun rikicin Boko Haram. Buhari zai kai ziyarar ne bayan kammala Azumin Ramadan.

Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari REUTERS
Talla

Ofishin shugaban na Najeriya ya tabbatar da ziyarar Buhari zuwa Kamaru idan an kammala Azumin watan Ramadan.

Shugaba Paul Biya dai ya kauracewa taron kasashen da ke makwabtaka da Najeriya da aka gudanar a Abuja kan matsalar Boko Haram, lamarin da wasu ke ganin dangantaka ce da ta yi tsami tsakanin kasashen biyu wadanda suka shafe shekaru suna takaddama kan yankin Bakassi.

Kamaru da Nijar da Chadi sun taimaka wa Najeriya kwato garuruwa da dama da Mayakan Boko Haram suka kwace.

Kuma yanzu Najeriya da Kamaru da Chadi da Nigar da Benin sun amince su kafa runduna ta musamman domin yakar Boko Haram da ke barazana ga kasashen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.