Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayi:ICC na neman Al-Bashir na Sudan ruwa a jallo
Wallafawa ranar:
Kunna - 15:37
Wata Kotu a kasar Afirka ta kudu ta bada umurnin hana shugaban kasar Sudan Umar Hassan al Bashir barin kasar bayan ya halarci taron shugabanin kungiyar kasahsen Afirka, ta AU, saboda bukatar ganin an gurfanar da shi a gaban kotun duniya dake neman sa ruwa a jallo.Akan wannan ne muka baku damar tofa albarkacin bakinku a cikin shirin jin ra'ayoyinku masu saurare tare da Umaimah Sani Abdul-mu'umin