Isa ga babban shafi
Ghana

Gobara ta hallaka sama da mutane 90 a Ghana

Akalla sama da mutane 90 ne, suka rasa rayukansu sakamakon wata gobara da ta tashi a wani gidan mai da ke birinin Accra na kasar Ghana.Gobarar ta tashi ne a lokacin da ake tafka wani ruwa kamar da bakin kwarya wanda ya tilastawa mutane fakewa a gidan man.

Ta'adin da Gobarar gidan mai na birnin Accra ya yi.
Ta'adin da Gobarar gidan mai na birnin Accra ya yi. RFI
Talla

Gobarar data fara tun acikin daran jiya laraba a unguwar Kwame Nkrumah ta yadu har zuwa muhallin mutane da ke kusa da gidan man.

A lokacin daya kai ziyara inda lamarin ya auke Shugaban kasar Ghana John Dramani ya bayyana Gobarar a mastayin mumunar bala’i daya samu kasar.

Rahotanin dai na cewa adaddin mamata ka iya zarce adaddin da aka fitar a yanzu, kuma masu aikin ceto na ta kai kawo domin kwashe gawarwakin mutane da suka kone.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.