Masar
Masar ta sako daya daga cikin 'yan jaridan Aljareezah da take tsare dasu
Hukumomi a kasar Masar sun saki daya daga cikin ‘yan jaridu uku dake gidan yarin kasar bayan ya kwashe kwanaki samada 400 a tsare, saboda zarginsa da taimakawa kungiyar ‘yan uwa musulmi.Peter Greste wanda dan jaridan tashan al jazeerah ne har ya isa birnin Larnaca na kasar Cyprus bayan sakin sa daga gidan yarin Tora dake Alkahira.Tashan Aljazeera yayi fatan za a sako sauran ‘yan jaridu biyu dake tsare.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: