Isa ga babban shafi
Libya

Masar zata jagoranci taron Libya

Kasar Masar zata jagoranci taron Ministocin harakokin wajen kasashen da ke makwabtaka da Libya game da rikicin kasar a ranar Litinin, bayan Mayakan sa-kai sun karbe ikon tashar jirgin sama a birnin Tripoli.

Wani gida da rikicin Mayakan Sa-kai ya tarwatsa a unguwar Wershavana a Tripoli
Wani gida da rikicin Mayakan Sa-kai ya tarwatsa a unguwar Wershavana a Tripoli Reuters
Talla

Wannan matakin na zuwa ne bayan gungun Mayakan Fajr sun kwace ikon tashar jirgin sama a Tripoli.

Mahukuntan Libya sun kasa samar da zaman lafiya a kasar tun lokacin da ‘Yan tawaye suka kawar da gwamnatin Marigayi Kanal Ghaddafi.

Masar zata jagoranci taron ne a birnin al Kahira wanda zai kunshi ministocin harakokin waje na kasashen Libya da Masar da Algeria da Tunisia da Sudan da Chadi da Nijar.

A watan Yuli an gudanar da irin wannan taron inda ministocin harakokin wajen wadannan kasashen suka yi kira ga bangarorin siyasar Libya su hau teburin sulhu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.