Isa ga babban shafi
Najeriya

Jonathan zai gana da iyayen 'yan matan Chibok a wannan talata

A wannan talata ake sa ran shugaban Tarayyar Najeriya Goodluck Jonathan zai gana karo na farko da iyayen ‘yan mata sama da 200 da kungiyar Boko Haram ta sace a garin Chibok da ke jihar Borno a arewa maso gabashin kasar.

Iyayen 'yan matan Chibok
Iyayen 'yan matan Chibok Reuters/Stringer
Talla

An dai jima ana yada jitar jitar cewa shugaban zai gana da iyayen ‘yan matan musamman ma bayan da mai fafutukar bunkasa ilimin mata a duniya wato Malala Yusafzai ‘yar kasar Pakistan ta neme shi da ya yi hakan.

Ba a dai san muhimman batutuwan da shugaban zai zanta da iyayen ‘yan matan ba wadanda suka share tsawon kwanaki kusan dari daya a hannun ‘yan kungiyar ta Boko Haram.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.