Isa ga babban shafi
Najeriya

Jonathan ya nada Shekarau Ministan Ilimi

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya nada wasu sabbin Ministoci guda hudu da suka hada da Tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau da Stephen Oru da Adedayo Adeyeye da Abdul Bulama, bayan Majalisa ta tantance su.

Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau
Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau
Talla

Jonathan ya nada Shekarau a matsayin Ministan Ilimi, Adeyeye karamin Ministan ayyuka, Oru a matsayin Ministan yankin Niger Delta sai Bulama a matsayin Ministan Kimiya da Fasaha.

Ana dai ganin wannan wasu matakai ne da shugaban na Najeriya ya dauka domin gina wadanda zasu yi masa yakin neman zaben shugaban kasa wa’adi na biyu, kodayake bai fito yace zai sake yin takara ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.