Mauritaniya ta sake zaben shugaba mai ci Muhammad Ould Abdel-aziz
Shugaban kasar Mauritanya Muhammad Ould abdel Aziz ya sake samun nasarar zaben shugaban kasar da aka gudanar a kasar. Sakamakon zaben dai ya nuna cewar shugaban ya samu sama da kashi 81 cikin 100 na kuri’un da ka jefa
Wallafawa ranar:
An dai bayyana sakamakon zaben ne bayan da abokan hamayyarsa suka bayyana kauracewa zaben da suka bayyana a matsayin abin kunya.
Muhammad Ould Abdel Aziz wanda ya karbi shugabancin kasar a Watan Agustan 2008 bayan wani juyin mulki da ya gudana a kasar da ke a yankin Arewacin Afruka, ya yi gangamin zabe mai tsananin gaske abinda ya kai shi ga samun kashi 81 da digo 89 cikin 100 na akasarin kuri’un da aka jefa.
Ko a sakamakon farko da Hukumar zaben kasar ta fitar a jiya Lahadi ta bayyana cewar Ould na da tazara mai nisa a gaba da sauran ‘yan takarar zaben, domin Ibrahim Moctar Sarr na da kashi 44.4 ne, a yayin da Lalla Mariem Mint Maulaye Idris mace guda kacal da ta tsaya takara a zaben, ke da kasa da kashi 1.
Akasarin masu jefa kuri’a dai kamar wani Dattijo mai shekaru 70 ya bayyana, sun ce zaben ya karkata ne ga yanda kasar a karkashin jagorancin muhammad Ould Abdel Aziz ta samu kubuta daga hare-haren masu tada kayar baya, halin da ta kasance a ciki shekaru da dama da suka gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu