Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya ta bude kofar tattaunawa da Boko Haram

A wata Ziyara da ya kai a garin Maiduguri, Babban hafsan rundunar Sojin Najeriya Laftanal Kanal Kenneth Minimah yace kofar tattaunawa da mayakan Boko Haram a bude take kamar yadda zasu iya yin amfani da karfi domin murkushe su.

Babban hafsan Sojin Najeriya Laftanal Janar  Kenneth Minimah
Babban hafsan Sojin Najeriya Laftanal Janar Kenneth Minimah Informationnigeria
Talla

Minimah ya fadi haka ne a lokacin da ya kai ziyara a Barikin Sojoji inda Mayakan Boko Haram suka kai hari domin jajantawa tare da karfafawa Sojoji kwarin gwiwa.

Akwai dai kwamitin da shugaba Goodluck Jonathan ya kafa domin tattaunawa da Boko Haram don kawo karshen kashe kashen rayukan mutane a Najeriya. kodayake shugaban Kungiyar ya fito a faifan Bidiyo yana yin watsi da tayin na sulhu

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.