Isa ga babban shafi
Nijar

Manyan jami'an Nijar sun gana da makiyan jihar Tillabery

Shugaban hukumar sauraron korafe-korafen ‘yan kasa a Jamhuriyar Nijar Shefou Amadou, ya gana da sarakunan gargajiya da kuma shugabannin kungiyoyin makiyaya da ke cikin jihar Tillabery kusa da iyakar kasar da Mali inda ake yawan samun tashe-tashen hankula a tsakanin al’umma.

Mahamadou Issoufou, shugaban kasar Nijar
Mahamadou Issoufou, shugaban kasar Nijar France 24
Talla

Ziyarar ta Shefou ta zo ne mako daya bayan da kungiyoyin makiyaya da ke zaune a yankin suka gabatarwa gwamnatin kasar da wata wasika da ke zargin cewa gwamnati ta kawar da kai dangane da irin matsalolin da makiyayan ke fama da su.

Shi dai yankin kan iyakar kasar ta Mali da jamhuriyar Nijar, yanki ne da ake yawan samun hare-hare daga ‘yan bindiga, wadanda ke kashe jama’a da kuma sace dabbobin makiyayan jamhuriyar Nijar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.