Rikicin Sudan ta Kudu
A ranar 15 ga watan Disemban 2013 ne rikici ya barke a Sudan ta kudu da ta balle daga Sudan a 2011 bayan Shugaba Salva Kiir ya zargi tsohon mataimakinsa da yunkurin kifar da gwamnatinsa a Juba. Yanzu rikicin ya rikide zuwa na kabilanci tsakanin Kabilar Dinka ta Salva Kiir da Kabilar Nuer ta Riek Machar.