Isa ga babban shafi
Mali

Mutane 4 sun mutu a yankin Kidal arewacin Mali

Rahotanni daga kasar Mali na cewa mutane Hudu ne suka rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu raunuka, lokacin da rikicin ya barke tsakanin Azbinawa jar fata da kuma sauran al’ummomi bakar fata a garin Kidal da ke arewacin kasar, yayin da wasu rahotannin ke cewa an kona babbar kasuwar garin.

Yankin Kidan a arewacin Mali
Yankin Kidan a arewacin Mali REUTERS/Stringer
Talla

Wannan na zuwa a dai dai lokacin da mahukuntan kasar ke shirye shiryen zaben shugaban kasa bayan kwato arewacin kasar daga hannun ‘Yan tawaye.

Ma’aikatar tsaron kasar Mali ta tabbatar da faurwar lamarin, inda ta ce an kona gidaje da kadarori da dama a wannan gari da ake kallo a matsayin babban sansanin kungiyar ‘yan tawayen da ke neman kafa kasar azbinawa wato MNLA.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.