Hukumar da ke kula da sufurin jiragen ruwa ta duniya tace an samu karuwar fashin jirage a tekun Guinea, wannan matsalar ce kuma ke ci wa kasashen Afrika tuwo a kwarya. Wannan ne dai ya sa Shugabanin Kasashen Afrika ta Yamma, da Afrika ta Tsakiya, suka gudanar da taronsu a Yaoundé a kasar Kamaru, inda suka dauki kudirin kafa rundunar da za ta yi yaki da ‘Yan fashin teku. Shirin Duniyarmu a Yau ya tattauna ne game da wannan batu da kuma illolinsa ga tattalin arzikin kasashen Afrika.