Matsalar Tsaro a Najeriya
A shekarar 2009 ne Kungiyar Jama'atu Ahlil sunnah Lid Da'awati wal Jihad da ake kira Boko Haram ta kaddamar da hare hare domin daukar fansan kisan da aka yi wa Shugabansu Muhammad Yusuf da mambobinsu, kuma tun a lokacin Najeriya ta fada cikin matsalar tsaro bayan gwamnatin Yar'adua ta yi wa tsagerun Niger Delta afuwa. Kungiyoyin kare Hakkin bil'adama sun ce sama da mutane 3,000 ne suka mutu tun fara kaddamar da hare haren kungiyar Boko Haram, tare da zargin Jami'an tsaro da kisan fararen hula da sunan farautar 'yan kungiyar.