Isa ga babban shafi
Mali

Shugaban Mali ya yi watsi da matakin tattaunawa da Ansar Dine

Shugaban rikon kasar Mali Dioncounda Traore, ya yi watsi da matakin zama teburin sasantawa da Mayakan Ansar Dine da suka karbe ikon yankin Arewaci tsawon watanni Tara, amma shugaban ya ce a shirye ya ke ya tattauna da ‘Yan tawayen Abzinawa.

Shugaban rikon kasar Mali, Dioncounda Traoré
Shugaban rikon kasar Mali, Dioncounda Traoré AFP/Habibou Kouyaté
Talla

Mista Traore ya shaidawa RFI cewa Gwamnatin shi a shirye ta ke ta shiga tattaunawa da wakilan Kungiyar ‘Yan tawayen Abzinawa ta MNLA, tare da watsi da duk wani matakin hawa teburin tattaunawa da Mayakan Ansar Dine.

Bayan karbe manyan biranen Arewacin kasar, Gao da Timbuktu da Kidal, Gwamnatin Faransa ta nemi a hau teburin tattaunawa da ‘Yan tawaye.

Kakakin ma’aikatar tsaron Faransa Philippe Lalliot, ya ce tattaunawa tsakanin Gwamnati da ‘Yan tawaye ita ce hanyar wanzar da zaman lafiya a Mali.

Amma Mista Traore yace zai iya tattaunawa da ‘Yan tawayen Abzinawa ba tare da Mayakan Ansar Dine ba wadanda ake alakantawa da kungiyar Al Qaeda.

A ranar 11 ga watan Janairu ne Faransa ta kaddamar da yaki a Mali domin kwato yankin Arewaci daga ikon Mayakan Ansar dine.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.