Isa ga babban shafi
mali

Shugaban kasar Mali zai kai ziyara Faransa

Shugaban rikon kwarya na kasar Mali Diacounda Trarore na shirin kai ziyarar aiki a birnin Paris na kasar Faransa a ranar laraba ta makon mako mai zuwa domin ganawa da shugaba Francois hollande.

Peu avant la nomination de Django Sissoko, le président Dioncounda Traoré avait accepté la démission de Cheick Modibo Diarra.
Peu avant la nomination de Django Sissoko, le président Dioncounda Traoré avait accepté la démission de Cheick Modibo Diarra. AFP PHOTO / HABIB KOUYATE
Talla

Sa’o’i kadan kafin sanar da hakan ne dai shugaban na Faransa wanda ke gabatar da jawabi ga jami’an diplomasiyya na kasashen duniya a birnin Paris,ya bayyana cewa a shirye kasarsa take ta taimaka domin a yaki ‘yan tawayen kasar Mali matukar dai kwamitin tsro na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da hakan.

Kawo yanzu dai babu karin bayani a game da muhimman abubuwan da shugaban na Mali da kuma na Faransa za su tattauna a kai, to amma ko shakka babu batun halin da ake ciki a arewacin Mali ne zai fi mamaye wannan ziyara ta shugaba Dioncounda Traore.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.