Isa ga babban shafi
Najeriya

‘Yan bindiga sun harbe kwamishinan Shari’a a Najeriya

‘Yan bindiga a Maiduguri, sun hallaka kwamishinan shari’ar Jihar Barno, Zanna Malam Gana, a kauyan sa dake Bama. Wannan na zuwa ne kwana guda bayan harin da aka kaiwa Tsohon shugaban gandirebobin Nigeria, Ibrahim Jarma a Azare, inda aka raunana shi, kana kuma aka hallaka dogarin sa. 

Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan
Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan
Talla

“Mun samu bayanan rasuwar kwamishinan shari’a Zannah Malam Gana, wasu mutane dauke da bindiga ne su ka harbe shi a gidansa da misalin 8:45 na yamma a daren jiya” inji wani Jami’in gwamnati.

Shi kuwa Shugaban gandirobobin, an kashe ne a Jihar Bauchi a yayin da ya ke barin masallaci zuwa gidansa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.