Isa ga babban shafi
Nijar

An sace tallafin ambaliyar ruwa a Nijar

Rahotanni daga Jamhuriyyar Niger na cewa an sace tallafin da gwamnatin kasar ta samu daga kasashen wajen domin tallafawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa. Rahotannin na cewa wadanda gwamnatin ta daurawa alhakin raba Tallafin ga mutane, su ne suka sace kayyakin.

Ambaliyar Ruwa a birnin Yamai
Ambaliyar Ruwa a birnin Yamai
Talla

Nijar ta samu tallafin abinci da ya kai Ton 6,300 daga kasashen waje bayan samun ambaliyar ruwa da ta yi sanadiyar mutuwar mutane 68 tare da raba miliyoyin mutane da gidajensu a watan Agusta.

Ministan cikin Gida Abduo Labo shi ne ya tabbatar da haka a gaban manema labarai. Kodayake bai ce ga adadin abinda aka sace ba.

Jamhuriyyar Nijar dai na daya daga cikin kasashen Yankin Sahel da ke fama da matsalar karancin Abinci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.