Kenya
A Kasar Mutane 10 Sun Mutu Sakamakon Zaizayar Kasa
A kasar Kenya mutane akalla 10 ne suka rasa rayukansu sakamakon zarzayar kasa, bayan wani ruwabn sama kamar da bakin kwarya. Kungiyar bada agaji ta Red Cross tace awannan shekaran jimillan mutanen da suka rasa rayukan su sun kai 100 sakamakon ambaliyar ruwa da zaizayar kasa.A watan jiya, a kasar Uganda an sami ambaliyar ruwa da tayi sanadiyyar mutuwar mutane da yawa.Zaizayar kasa a Kasar Kenyan ta auku ne ayankin kauyen Kitony na gunduman Marakwet dake yammacin kasar ta Kenya.Kungiyar ta Red Cross dai ta kaddamar da aikin bada agaji a wannan yanki.
Wallafawa ranar: